- Himmatuwar sahabbai - Allah Ya yarda da su - da kuma tsoronsu daga abinda ke tare da su na ayyukan Jahiliyya (da suka yi a baya).
- Kwadaitarwa akan tabbata akan Musulunci.
- Falalar shiga addinin Musulunci, kuma cewa shi yana kankare ayyukan da suka gabata.
- Wanda ya yi ridda da munafiki za’a yi masa hisabi da dukkanin wani aikin da ya gabatar a lokacin Jahiliyya, haka ma kuma da dukkanin wani zinibin da ya aikata shi a cikin Musulunci.