/ Wanda ya zo wa matarsa ta duburarta tsinanne ne

Wanda ya zo wa matarsa ta duburarta tsinanne ne

Daga Abu Huraira - Allah Ya yarda da shi - ya ce: Manzon Allah - tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi - ya ce: "Wanda ya zo wa matarsa ta duburarta tsinanne ne".

Bayani

Annabi - tsira da amincin Allah su tabbata agare shi - ya tsoratar daga miji ya zo wa matarsa ta duburarta; cewa shi tsinanne ne abin korewa daga rahamar Allah, kuma shi babban laifi ne cikin manyan laifuka.

Hadeeth benefits

  1. Haramcin zakkewa mata ta duburarsu.
  2. Jin daɗi daga mata a koma bayan duburarta na jikinta ya halatta.
  3. Musulmi yana zakkewa mace ne ta farjinta kamar yadda Allah Ya umarce shi; amma ta dubura to a cikin hakan akwai ɓata ɗabi'a, da tozarta zuriya, da saɓawa abinda nagartattun ɗabi'u suke a kansa, da kuma cutuka masu kaiwa ga ma'auratan.